Translations:Baptism/17/ha

Yesu ya umurce almajiransa su je su almajirantad da dukan al’umai sunayi masu Baptisma a cikin sunan Allah Uba da Da da Ruhu Mai Tsarki. Su kuma koya wa mutane yin biyaya da duk abubuwanda ya koya masu. Almajiran sun yi duk kamar yadda Yesu ya umurce su, duk inda sun tafi, suna yin baptisma ma wadanda sun karbi Yesu.