Translations:Baptism/19/ha
Mu furta zunubanmu mu kuma juyo daga garesu. Kadda mu boye zunubanmu mu palashe su (1Yahaya 1:9). Mu yi furci a inda mun sani ba mu yi daidai da nufin Allah ba. Mu roke Allah ya gafarta mana, mu kuma dakatar da kanmu daga yin zunubi. Da taimakon Allah zamu chanza halayenmu mu kuma bi Nufin Allah.